Kamfanin dillancin labaran iqna ya bayar da rahoton cewa, a cikin makonni biyu masu zuwa ne za a gudanar da taron girmama mahardata da makaranta kur’ani mai tsarki wanda makarantar Tanzil ta shirya da ke garin Port na kasar Australia a jihar yammacin kasar.
A yayin wannan taro dai za a gayyaci fitattun mahardata da makaranta daga sassa daban-daban na kasar da ma kasashen ketare.
Haka nan kuma za a bayar da kyatuka na musamman ga masu hidima ga kur’ani mai tsarki, kama daga malamai, da mahardata da kuma makaranta.
Wannan dais hi ne karo na farko da za a fara gudanar da irin wannan taro wanda makarantar za ta dauki nauyinsa, wanda kuma ake sa ran zai ci gaba da gudana a kowace shekara.