IQNA

An Karyata bayanan da Ke Cewa Yahudawa Sun sake  Rufe Babu Rahma

23:49 - February 23, 2019
Lambar Labari: 3483397
Bangaren kasa da kasa, Sheikh Ikrama Sabri babban limamin quds ya karyata batun cewa yahudawa sun sake rufe babau rahma.

Kamfanin dillancin labaran iqna ya ahbarta cewa, a yau Sheikh Ikrama Sabri babban limamin quds ya karyata batun cewa yahudawa sun sake rufe masallacin babau rahma da ke gefen masallacin aqsa mai alfarma.

Ya ci gaba da cewa, tun bayan da Isra'ila ta rufe wannan wuri mai albarka tun kimanin shekaru goma sha shida da suka gabata,a  yanzu Falastinawa sun samu nasar bude shi, kuma zai ci gaba da kasancewa a bode.

Tun bayan bude masallacin bbu rahma a jiya, ake ta yada wasu bayanai marassa tushe kancewa Isra'ila ta sake rufe wurin, bayanan da malaman quds suka karyata.

3792600

 

 

captcha