IQNA

Markel: Ba Za Mu Shiga Cikin Duk Wani Hari Da Za A Kai Kan Syria Ba

23:51 - April 13, 2018
Lambar Labari: 3482566
Bangaren kasa da kasa, shugabar gwamnatin kasar Jamus Angela markel ta bayyana cewa, kasarta ba za ta shiga cikin duk wani shirin kaddamar da harin soji a kan kasar Syria ba.

Kamfanin dillancin labaran iqna ya habarta cewa, a lokacin da take yin magana a jiya shugabar gwamnatin kasar Jamus Angela Mrkel ta bayyana cewa, kafin daukar duk wani matakin soji a kan Syria, dole ne a yi bincike a dukkanin bangarori.

Ta kara da cewa, a iyakacin sanina dai har yanzu ba a yanke mataki na karshe ba kan batun kaddamar da hari kan kasar Syria.

Markel ta jaddada cewa, wajibi ne kasashen turai su tababtar da cewa bakinsu ya zo daya kafin daukar duk wani matakin soji a kan Syria, kuma muna jiran sauran sauran kasashen turai da suke da wannan aniya da su shawara da mu.

A ranar Laraba da ta gabata ce dai shugaban Amurka Donald Trump ya yi barazanar kai hari kan kasar Syria, bisa zargin cewa gwamnatin kasar ta yi amfani da makaman nukiliya kan ‘yan ta’adda, amma Rasha ta mayar da martini da cewa za ta kakkabo duk wani makami da Amurka za ta harba a kan Syria.

3705298

 

 

 

 

 

captcha