Asep Saifuddin shi ne shugaban jami'ar reshen Azhar da ke kasar Indonesia, ya bayyana cewa babbar manufar shirya zaman taron dai ita ce, fitar da sabbin hanyoyi na bunkasa karantarwar addinin muslunci.
Bayanin ya ci gaba da cewa, kasar Indonesia na daga cikin kasashen musulmi da a halin yanzu suke samun ci gaba cikin sauria dukkanin bangarori na yada addinin muslunci da koyarwarsa.
Da dama daga cikin wadanda suka halrci taron sun bayyana wajbcin yin amfani da hanyoyi na ilmantarwa da zasu dakushe yunkurin wasu masu yada akidar ta'addanci da sunan muslunci da suke kafirta musulmi suna kiransu mushrikai ko 'yan bidi'a.