Kamfanin dillancin labaran iqna ya nakalto daga shafin Daily Sabah cewa, an gudanar da wannan jerin gwano a garin Muzaffar Abad na Kashmir, inda aka yi tir da abin da India take yi kan yankin Kashmir da ke akrkashinta.
Wannan zanga-zanga ta zo ne kwana daya bayan furucin da firayi ministan kasar wanda ya bayyana cewa dole ne a dauki mataki na ganin an cewa an takawa India burki kana bin da take tafkawa a kasar al’ummar Kashmir.
A ranar 27 ga watan Satumba ne firayi ministan kasar Pakistan zai gabatar da bayani a gaban babban taron majalisar dinkin duniya, inda zai yi bayani kana bin da yake faruwa a Kashmir.
Batun rikicin Kashmir dai ya kawo rashin jituwa tsakanin Pakistan da India.